BANKIN DUNIYA DA MASANA SUN YI KIRA A ƘARA KASAFIN ILIMIN YARA ’YAN GUDUN HIJIRA A NAJERIYA
BANKIN DUNIYA DA MASANA SUN YI KIRA A ƘARA KASAFIN ILIMIN YARA ’YAN GUDUN HIJIRA A NAJERIYA
By
Umar Nusaiba Ibrahim
Bankin Duniya tare da wasu ƙwararru sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da masu zaman kansu da su ƙara saka hannun jari wajen ilimi, kiwon lafiya da abinci mai gina jiki ga yara ’yan gudun hijira a Najeriya.
Sun bayyana hakan ne a taron Africa Social Impact Summit da aka gudanar a Legas, inda suka ce kula da yara tun suna ƙanana na taimakawa wajen rage talauci da kuma gina ingantaccen jarin ɗan Adam na ƙasa.
Babbar ƙwararriyar Bankin Duniya kan harkokin lafiya, Dakta Ritgak Tiiley-Gyado, ta ce yara da ke sansanonin ’yan gudun hijira bai kamata a hana su ilimi da sauran muhimman ayyukan jin daɗin rayuwa ba, domin su ne makomar Najeriya.
A nasa jawabin, Kodinetan Nigeria Coalition on Early Childhood Development in Crisis, Arome Agenyi, ya nuna damuwa cewa kusan kashi ɗaya cikin ɗari (1%) ne kawai na kasafin kuɗin ilimi ake warewa domin ilimin yara ƙanana. Ya yi kira ga gwamnati da kamfanoni masu zaman kansu su ƙara zuba jari domin kauce wa rasa wata gaba ɗaya ta yara.
Sauran mahalarta taron sun jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da masu zaman kansu, tare da samar da isasshen abinci da kuɗaɗen tallafi domin tabbatar da cewa yara, musamman waɗanda rikici ya shafa, sun samu ingantaccen ilimi da kyakkyawar makoma.
#NexViewNews #WorldBank #IDPs #Education #EarlyChildhoodDevelopment #Nigeria #ChildEducation #NorthEast #HumanCapital #UNHCR #SterlingOneFoundation #PlanInternational #AfricaSocialImpactSummit

Comments
Post a Comment