ABU Ta Fara Binciken Takardun Karatun Farfesa Abdullahi Abubakar


 

ABU Ta Fara Binciken Takardun Karatun Farfesa Abdullahi Abubakar


Daga Umar Nusaiba Ibrahim 


Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya (ABU) ta fara bincike kan sahihancin takardun karatun wani farfesa a jami’ar, Arc. Abdullahi Abubakar, bayan wasu bayanai da suka yaɗu a kafafen sada zumunta sun jawo ce-ce-ku-ce.


Rahotannin da suka yaɗu sun nuna cewa farfesan na da digirin PhD guda biyar, digirin Master guda biyar, digirin farko guda bakwai da difloma 11, lamarin da ya jawo hankalin jama’a.


Daraktan Hulɗa da Jama’a na ABU, Awwal Umar, ya tabbatar da cewa jami’ar na sane da batun, tana kuma gudanar da binciken da ya dace domin tabbatar da sahihancin bayanan.


Ya ce ABU ba za ta yi gaggawar yanke hukunci ba, inda ta bayyana cewa za ta sanar da matsayinta a hukumance bayan kammala binciken da kuma tabbatar da sahihan bayanai.


A nasa bangaren, Farfesa Abdullahi Abubakar bai amsa kiran waya da aka yi masa ba, amma ya tabbatar da samun saƙon neman jin ta bakinsa, inda ya ce ba zai yi tsokaci kan batun a yanzu ba.


#AhmaduBelloUniversity #FarfesaAbdullahiAbubakar #Bincike #TakardunKaratu #Ilimi #JamiA #Nigeria #NexviewTV

Comments

Popular posts from this blog

Gunshots As Rival Cult Groups Clash At Rivers Varsity

17 Bandits, 10 Police Officers Killed In Zamfara-Kebbi Clash

Opposition Lawmakers Protest As Reps Pass State Police Bill