FAAC: Gwamnonin Jihohi Na Fuskantar Tambayoyi Kan Yadda Suka Kashe N47.25tn Cikin Shekaru Uku


 

FAAC: Gwamnonin Jihohi Na Fuskantar Tambayoyi Kan Yadda Suka Kashe N47.25tn Cikin Shekaru Uku


Umar Nusaiba Ibrahim 


Gwamnonin jihohin Najeriya 36 na fuskantar ƙarin matsin lamba da tambayoyi kan yadda suka kashe kuɗaɗen da suka samu daga Asusun Tarayya, FAAC, bayan wani sabon rahoto ya nuna cewa gwamnatin tarayya, jihohi da ƙananan hukumomi sun raba kusan N47.25 tiriliyan a cikin shekaru uku daga 2023 zuwa 2025.


Bayanan da Ma’aikatar Kuɗin Najeriya ta fitar sun nuna cewa jimillar kuɗaɗen da matakan gwamnati uku suka samu daga FAAC tsakanin 2017 zuwa 2025 sun kai N93.13 tiriliyan. Sai dai sama da rabin wannan kuɗi, wato N47.25 tiriliyan, an raba shi ne a cikin shekaru uku bayan cire tallafin man fetur da wasu sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta aiwatar.


Adadin kuɗin da ake rabawa ya ƙaru sosai daga N10.09 tiriliyan a 2023, zuwa N15.26 tiriliyan a 2024, sannan ya kai sabon tarihi na N21.90 tiriliyan a 2025. Jihohi sun kasance cikin waɗanda suka fi cin gajiyar ƙarin kuɗin, inda rabonsu ya ƙaru daga N4.18 tiriliyan a 2023 zuwa N8.93 tiriliyan a 2025.


Sai dai masana tattalin arziki da ƙungiyoyin farar hula na cewa ƙarin kuɗaɗen da gwamnatoci ke samu bai haifar da sauƙin rayuwa daidai da yadda ake tsammani ba, musamman ganin yadda farashin kayayyaki, rashin aikin yi, talauci da matsalolin ababen more rayuwa ke ci gaba da ƙaruwa. Wasu masana sun bukaci gwamnonin su fi mayar da hankali kan kiwon lafiya, ilimi, ruwa, hanyoyi, aikin yi da sauran ayyukan da za su amfani talakawa kai tsaye.


Masana sun kuma yi kira da a ƙara bayyana yadda ake amfani da kuɗaɗen FAAC, tare da bai wa ‘yan ƙasa da ƙungiyoyin farar hula damar bibiyar ayyukan da ake gudanarwa. Sun ce ƙarin kuɗin da jihohi ke samu ya kamata ya bayyana a rayuwar jama’a ta hanyar inganta ayyukan gwamnati da rage matsin tattalin arziki, maimakon kashe kuɗi kan ayyukan da ba su da tasiri kai tsaye ga rayuwar talakawa.


#FAAC #Nigeria #Governors #Revenue #Tinubu #States #Economy #NexviewTV

Comments

Popular posts from this blog

Gunshots As Rival Cult Groups Clash At Rivers Varsity

17 Bandits, 10 Police Officers Killed In Zamfara-Kebbi Clash

Opposition Lawmakers Protest As Reps Pass State Police Bill