KACRAN Ta Yaba wa Yobe Kan Zaman Lafiya Tsakanin Manoma da Makiyaya


 

KACRAN Ta Yaba wa Yobe Kan Zaman Lafiya Tsakanin Manoma da Makiyaya


Daga Umar Nusaiba Ibrahim 


Ƙungiyar Makiyaya ta Kulen Allah ta Najeriya, KACRAN, ta bayyana cewa jihar Yobe ba ta fuskanci wani babban rikicin manoma da makiyaya da ya haddasa asarar rayuka ko lalata dukiya ba tun bayan fara kakar noman shekarar 2026.


Ƙungiyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar bayan gudanar da wani taron wayar da kan jama’a a Damaturu, babban birnin jihar. KACRAN ta ce ƙara samun fahimtar juna da haɗin kai tsakanin manoma da makiyaya, da kuma ƙoƙarin gwamnatin jihar wajen tabbatar da zaman lafiya, sun taimaka matuka wajen dakile manyan rikice-rikice.


KACRAN ta yi kira ga manoma da su guji kutsawa ko yin noma a wuraren kiwo da aka tanada, da kuma hanyoyin da dabbobi ke bi. Haka kuma, ta buƙaci makiyaya da su guji shiga gonakin da aka shuka ko barin dabbobinsu su lalata amfanin gona.


Ƙungiyar ta kuma shawarci ɓangarorin biyu da su riƙa kai rahoton duk wata matsala da ta taso ga hukumomin da abin ya shafa, maimakon ɗaukar doka a hannu ko yanke hukunci cikin gaggawa ba tare da bin ƙa’ida ba.


A yayin da take yabawa Gwamna Mai Mala Buni, sarakunan gargajiya, shugabannin ƙananan hukumomi da jami’an tsaro kan rawar da suke takawa wajen tabbatar da zaman lafiya, KACRAN ta yi kira ga sauran gwamnonin jihohi da su yi koyi da tsarin Yobe wajen magance rikicin manoma da makiyaya cikin lumana.


Ƙungiyar ta ce yin hakan zai taimaka wajen ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai tsakanin al’ummomi, musamman yayin da Najeriya ke tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.


#KACRAN #Yobe #ManomaDaMakiyaya #ZamanLafiya #Aminci #Damaturu #MaiMalaBuni #TsaronKasa #HaɗinKai #Noma #Kiwo #Nigeria #Zaben2027 #NexviewTV

Comments

Popular posts from this blog

Gunshots As Rival Cult Groups Clash At Rivers Varsity

17 Bandits, 10 Police Officers Killed In Zamfara-Kebbi Clash

Opposition Lawmakers Protest As Reps Pass State Police Bill