Mutum Biyar Da Ake Zargin ’Yan ISWAP Ne Sun Mutu Sakamakon Fashewar Bam A Borno


 Mutum Biyar Da Ake Zargin ’Yan ISWAP Ne Sun Mutu Sakamakon Fashewar Bam A Borno


Daga Umar Nusaiba Ibrahim 


Mutum biyar da ake zargin mambobin ƙungiyar ISWAP ne sun mutu bayan wani bam ya fashe a lokacin da suke haɗa na’urorin fashewa (IED) a ƙauyen Maina Daya da ke ƙaramar hukumar Marte a Jihar Borno.


Rahotanni sun ce waɗanda suka mutu sun haɗa da wani jami’in lafiya na ƙungiyar, ƙwararrun masu haɗa bama-bamai guda biyu daga ƙasashen Larabawa, da kuma wasu ƙwararrun masu kera bama-bamai na ISWAP guda biyu.


Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa fashewar ta faru ne yayin da ake shirya bama-baman da ake zargin za a kai hare-hare da su a kan hanyoyin sojoji.


Masana harkokin tsaro sun ce wannan lamari na iya rage ƙarfin ISWAP na kai hare-haren bama-bamai na ɗan wani lokaci, yayin da rundunar Operation HADIN KAI ta ƙara tsaurara sintiri da hare-haren da take kai wa a yankunan Monguno, Marte da Gamboru Ngala domin hana ƙungiyar sake farfaɗowa.



#Borno

#ISWAP

#OperationHadinKai

#Tsaro

#YakiDaTaaddanci

#NigerianArmy

#Marte

#Monguno

#BreakingNews

#NexviewTV

Comments

Popular posts from this blog

Gunshots As Rival Cult Groups Clash At Rivers Varsity

17 Bandits, 10 Police Officers Killed In Zamfara-Kebbi Clash

Opposition Lawmakers Protest As Reps Pass State Police Bill