Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Alkawarin Samun Mafita Cikin Shekara Ɗaya
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Alkawarin Samun Mafita Cikin Shekara Ɗaya
Umar Nusaiba Ibrahim
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya ce zai kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro a Najeriya cikin shekara guda idan aka zaɓe shi a zaben 2027.
Atiku ya bayyana hakan ne a wata hira da BBC Hausa, inda ya ce gwamnatinsa za ta ƙara yawan jami’an tsaro tare da samar musu da kayan aiki da isasshen kuɗin gudanar da ayyukansu.
Ya kuma ce za a tallafa wa matasa da jari domin su kafa sana’o’i, yana mai cewa rashin aikin yi na daga cikin abubuwan da ke sanya wasu matasa shiga aikata laifuka.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya kuma yi alkawarin ƙarfafa haɗin gwiwar sojojin ƙasashen ECOWAS, tare da ƙoƙarin dawo da ECOMOG domin taimakawa wajen magance matsalar tsaro a yankin.
Game da zaben 2027, Atiku ya nuna shakku kan INEC, amma ya bukaci ’yan Najeriya su fito ƙuri’a, su kare ƙuri’unsu kuma su tabbatar an ƙidaya su yadda ya kamata.
#AtikuAbubakar #2027Election #RashinTsaro #Tsaro #Nigeria #ADC #ECOWAS #INEC #SiyasarNajeriya #NigerianPolitics

Comments
Post a Comment